KanunLabarai

Da Dumi-Dumi! Ana Shirin Tsige Ganduje Daga Shugabancin APC

Alamomi masu karfi sun bayyana kan yunkurin tsige Shugaban Jam’iyyar APC na Kasa, Abdullahi Ganduje, daga kujerarsa.

Alfijir labarai ta rawaito majiyoyi sun ce wasu masu ruwa da tsakin APC daga yankin Arewa ta Tsakiya da na hannun damansu ne suke kokarin raba Ganduje da kujerar domin ta koma yankin.

Wasu rahotanni sun bayyana yadda tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, yake neman goyon bayan masu ruwa da tsaki domin darewa kan kujerar shugaban jam’iyyar APC.

Hotunan Yahaya Bello na neman shugabancin APC dai sun karade Abuja, awa 48 da saukarsa daga kujerar gwamna, kuma a daidai lokacin da jami’yyar ke shirin gudanar da babban taronta na kasa.

Abdullahi Adamu ya yi murabu ne sakamakon rikicin cikin gidan jam’iyyar, wanda wasu ke zargin yana da alaka da rashin goyon bayansa ga takarar Shugaba Bola Tinubu a zaben 2023.

Zaman Ganduje shugaban APC abi yi wa masu ruwa da tsakin Arewa ta Tsakiya dadi ba, kasancewar daga yankin Abdullahi Adamu ya fito, don haka suke ganin daga nan ya makata a samu wanda zai karashe wa’adinsa.

Wakilinmu ya yi kokarin jin ta bakin sakataren yada labaran APC na kasa, Felix Morka, kan wannan dambarwa, amma wayarsa ba ta shiga.

Source: Aminiya

Domin samun sahihan labarai shiga WhatsApp group na labarangariyawaye

https://chat.whatsapp.com/DJEjSDGhJeX3PHx7XzXeHx

Torawa Yan'uwa Da Abokai

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *