KanunLabarai

EFCC ta bankado yadda kungiyoyin addini ke hada-hadar kudaden haram ga ‘yan ta’adda

Shugaban Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC), Ola Olukoyede, ya ce hukumar ta gano wani kudiri na hada-hadar kudaden haram da wata kungiyar addini keyi ga ‘yan ta’adda.

Olukoyede, wanda ya bayyana hakan a wata tattaunawa ta yini daya kan “Matasa, Addini, da Yaki da Cin Hanci da Rashawa.” A ranar Larabar da ta gabata a Abuja, ya kuma ce an gano wasu kudaden da aka samu daga wata kungiyar addini ta Naira biliyan 7.

Ya ci gaba da cewa, EFCC ta gano kungiyoyin addini, cibiyoyi, kungiyoyin da ke da hannu wajen karkatar da kudade a kasar nan.

Olukoyede ya ce daya daga cikin irin wadannan kungiyoyin addini ta kai hukumar gaban kotu domin ta kare shugabanta bayan an bankado kudaden da aka bankado a asusun bankin sa.

Shugaban na EFCC ya ce kungiyar addini ta samu umarnin kotu da ya hana hukumar gayyato wa ko kamawa ko gurfanar da shugabanta.

“Ba za mu yi kasa a gwiwa ba wajen kwato kudaden da aka sace,” in ji Olukoyede.

“Abin bakin ciki ne yadda na tsaya a gaban manyan jama’a a yau, kasancewar kwarewarmu a yaki da cin hanci da rashawa yana da alaka da shugabannin addini da ma sarakunan gargajiya.

“Kamar yadda na tsaya a gabanku akwai batun da muke tafiyar da sama da biliyan 30 daga Najeriya, kuma mun iya gano Naira biliyan 7 ga wata kungiya ta addini.

“Kamar yadda muka rubuta wa shugaban wasika, abu na gaba da muka gani shi ne dokar hana mu gayyace su, tare da hana mu kwato kudaden.”

Sai dai ya ce hukumar EFCC ta daukaka kara kan hukuncin.

“A wasu lokutan da suka gabata, mun yi bincike kan batun karkatar da kudade, a wani wuri a kasar nan.

Olukoyede ya kara da cewa “Akwai wata kungiya ta addini da ke da alaka da hada-hadar kudaden haram ga ‘yan ta’adda, wadannan su ne matsalolin da muke fama da su.”

Ya kuma bayyana cewa tun bayan da ya hau kan karagar mulki kimanin watanni uku da suka gabata, hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta samu laifuka 747, amma ya ce sama da kashi 60 cikin 100 na laifukan laifukan da suka shafi yanar gizo ne.

“Ga shugabannin addininmu, kira na shi ne cewa wadanda ke jagorantar al’ummarmu daga coci-coci da masallatai su samar da sakonnin da ke daukaka masana’antu, aiki tukuru, jin dadi da wadatar arziki, ba tare da la’akari da yadda aka yi ta ba.

Domin samun sahihan labarai shiga WhatsApp group na labarangariyawaye

https://chat.whatsapp.com/DJEjSDGhJeX3PHx7XzXeHx

Torawa Yan'uwa Da Abokai

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *