KanunLabarai

Gwamnatin Kogi Za Ta Samar Da Doka Domin Yin Jarrabawa a Kyauta ga Daliban firamare da na Sakandire 

Credits photo kogi reporters Facebook page

A ranar Asabar din da ta gabata ne gwamnatin Kogi ta ce ta kammala shirye-shiryen biyan kudaden jarrabawar waje da ta cikin gida kyauta, a matsayin manufar gwamnatocin da za su biyo baya a jihar.

Kwamishinan Ilimi, Kimiyya da Fasaha na jihar, Mista Wemi Jones, ne ya bayyana hakan a wani taron kwamitin zartarwa na kungiyar shugabannin makarantun sakandire ta Najeriya (ANCOPSS) na yankin Arewa ta tsakiya a Lokoja.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, a watan Nuwamba 2023, gwamnatin Kogi ta ba da sanarwar bayar da ilimi kyauta ga dalibai tun daga firamare zuwa sakandare.

NAN ta ce wani muhimmin bangare na tsarin shi ne biyan kudin jarrabawar cikin gida da waje da gwamnatin jihar ta yi wa dalibai.

Jones ya ce dokar idan aka amince da ita, za ta tilasta wa Gwamnatin Kogi biyan kudin jarrabawar ciki da waje ga daliban da ke makarantun gwamnati a jihar.

Ya godewa kungiyar ANCOPSS ta jihar bisa hadin kan da take bayarwa wajen aiwatar da manufofin gwamnatin jihar da nufin samar da ingantaccen ilimi ga ‘yan jihar Kogi.

Kwamishinan ya jaddada cewa gwamnati na shirin tara daliban da za su yi takara a duniya a kowane fanni.

Ya bayyana cewa kafa Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Confluence (CUSTECH), Osara, da Jami’ar Jihar Kogi KSU Kabba, shi ne horar da dalibai a fannin kimiyya da fasaha.

A cewarsa, kafa cibiyoyin kuma shine don samar da damammaki ga daliban Kogi don samun damar karatun jami’a.

“Don cin gajiyar albarkatun kasa da ke da yawa a jihar, gwamnati na mai da hankali kan ilimin Kimiyya, Fasaha, Injiniya da Lissafi (STEM).

“GYB Model Science Secondary Schools da ake ginawa a fadin jihar ana nufin horar da dalibai don fuskantar kalubalen da ke gaba,” inji shi. (NAN)

Jones ya bayyana cewa, duk nasarorin da aka samu a fannin ilimi ba za su samu ba, in ba da jajircewar Gwamna Yahaya Bello ba, inda ya bayyana shi a matsayin Masihu da Allah ya aiko domin farfado da ilimi a Kogi.

Ya ce ilimi a matsayinsa na ginshikin ci gaban al’umma, an ba shi kulawar da ya kamata gwamna.

(NAN)

 

Torawa Yan'uwa Da Abokai

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *