KanunLabarai

Gwamnan Wata Jaha a Nijeriya ya hana sayar da abinci da amfanin gona ga wasu jihohin Kasar

Photo credits: Dawanau market Facebook page

Gwamnan jihar Neja, Mohammed Umar Bago ya sanya dokar hana sayarwa da raba kayan abinci da sauran amfanin gona a jihar zuwa wasu jihohin Najeriya na wucin gadi.

Gwamnan ya ba da wannan umarni ne a ranar Alhamis yayin da yake mayar da martani ga wata gagarumar zanga-zanga da ta afku a babban birnin jihar a Minna, babban birnin jihar don nuna adawa da hauhawar farashin kayayyaki da kuma tabarbarewar tattalin arziki a Najeriya.

A cewarsa, zanga-zangar ta biyo bayan wani labarin da ba daidai ba ne da ke ikirarin cewa gwamnati na shirin tara wasu kayayyakin abinci a jihar duk da tsananin yunwar da mutane ke fuskanta.

Gari ya waye ta rawaito kalaman gwamna kamar haka “Ya kamata a dakatar da manyan motocin da ke zuwa yin kiliya ko sayen kayan abinci daga mutanen kauyenmu da yawa a yanzu. Mun dakatar da sayan jama’a daga kasuwannin kananan hukumominmu, a dukkan kananan hukumomin mu daga yanzu har sai an samu labari. Duk wanda aka samu yana yin haka, mun baiwa jami’an tsaro da su ci gaba da kwace wadannan manyan motocin tare da raba abincin ga jama’a.”

Hotunan bidiyo a ranar Litinin sun nuna yadda masu zanga-zangar suka toshe manyan tituna yayin da suke korafin cewa babu wani yunkurin da gwamnati keyi domin rage wahalar da ake ciki na tsadar kayan abinci.

An dai ji masu zanga-zangar suna rera wakokin zanga-zangar, yayin da jami’an tsaro ciki har da ‘yan sanda suka sa ido akan su

A halin da ake ciki kuma, shugaba Bola Ahmed Tinubu ya umurci ma’aikatar noma da samar da abinci da ta saki kimanin tan dubu arba’in da biyu na hatsi da suka hada da masara, gero da garri.

Hakazalika, kungiyar Rice Millers ta Najeriya ta kuma kuduri aniyar gaggauta sakin sama da tan dubu sittin 60,000 na shinkafa ga jama’a.

Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a na kasa, Mohammed Idris ne ya bayyana hakan bayan taron kwamitin shugaban kasa kan matsalar abinci na gaggawa a ranar Alhamis a Abuja.

Domin samun sahihan labarai shiga WhatsApp group na labarangariyawaye

https://chat.whatsapp.com/DJEjSDGhJeX3PHx7XzXeHx

 

Torawa Yan'uwa Da Abokai

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *